Type Here to Get Search Results !

Iran ta sa ladan dala miliyan 80 ga duk wanda ya halaka Donald Trump

Kasar Iran ta saka ladan Dala miliyan tamanin $80 ga duk wanda ya halaka shugaban Amurka Donald Trump. Wannan ya biyo bayan kalaman Trump na cewa Amurka za ta kai wa kasar Iran mumunar hari matukar ta taba maradunta a harin ramuwar gayya.

Gidan Talabijin na kasar Iran ta bayar da sanarwar haka , tana mai cewa " Iran tana da mutane miliyan 80 bisa kididdigan yawan jama'an kasar Iran. Idan jama'a za su tara dala daya kowannensu za a sami dala miliyan tamanin  $80 kenan domin bayarwa ga duk wanda ya halaka Trump"

Wannan ya zo daidai da lokaci da ake gudanar da jana'izan Janar Qassem Soleimani da kasar Amurka ta kashe bisa umarnin shugan Amurka Donald Trump.

Jiragen tuka kanka na kasar Amurka sun harba makami mai linzami a kan motar Janar Qassem Soleimani wanda haka ya zama sanadin ajalinsa.

DAGA ISYAKU.COM Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp https://chat.whatsapp.com/DTV1WsH2ypv0WtRujXbA0F SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA Facebook.com/isyakulabari Twitter.com/isyakulabari

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN