An gano sunayen matattun ma'aikatan gwamnati 596 da ake biya albashi a jihar Bauchi

Gwamnatin jihar Bauchi ta gano ma'aikatan gwamnatin jihar guda 596 da suka mutu kuma ana biyan albashinsu da alawu har tsawon shekaru.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa Gwamnatin jihar Bauchi ta bankado fiye da ma'aikata 41,448 da ke karbar albashi daga gwamnatin jihar alhalin basu da lambar tantancewa na Banki watau BVN.

Gwaman jihar Bauchi Bala Muhammed, ya nada wani kwamiti da zai yi bincike a kan lamarin. Shugaban kwamitin Adamu Gumba ya shaida wa manema labarai sakamakon tantancewa da suka yi.

DAGA ISYAKU.COM Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp https://chat.whatsapp.com/DTV1WsH2ypv0WtRujXbA0F SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA Facebook.com/isyakulabari Twitter.com/isyakulabari
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN