Type Here to Get Search Results !

Hotunan yadda mata suka dinga kuka suna birgima a titi bayan cire Ihedioha daga mulki

Magoya bayan tsohon Gwamnan jihar Imo Emeka Ihedioha, sun bazama kan titin babban birnin jihar, watau Owerri , ranar Lahadi suna la'antar hukuncin Kotun koli da ya kori Ihedioha daga kujerar mulkin jihar.

Ranar Talata da ta gabata ne Kotun koli ta Najeriya ta soke nassarar da INEC ta ba Emeka Ihedioha na jam'iyar PDP, ta kuma mika wa Hope Ozodinma na jam'iyar APC.

Magoya bayan Ihedioha sanye da bakaken tufafi, sun kwanta a kan titi maza da mata suna kuka, tare da birgima. Wasu kuma suna rike da kwalaye da aka rubuta " Muna bukatar ya dawo" da " An halaka dimokaradiya"  sai " Ihedioha dai muka sani" da sauransu.


DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/DTV1WsH2ypv0WtRujXbA0F

Domin aiko labari, shawara ko tuntubarmu
LATSA NAN

SHAFUKANMU NA SADA ZUMUNTA

Facebook.com/isyakulabari

Twitter.com/isyakulabari

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN