Gawar Aisha (Cididu) |
Yan agaji na rufe kofar inda Aisha ta rasu kafin a dauki gawarta |
Mujallar ISYAKU.COM ya tabbatar da haka bayan wata gajeruwaar ganawa da wata tsohuwa mai suna Igen Na'uwa da ke unguwar Tudun wada a garin Birnin kebbi wacce ganau ce ba jiyau ba da lamarin ya faru a gabanta, ta shaidaa mana cewa;
Wasu mata da Aisha ke tar da su a bakin kofar shiga Masallaci kafin rasuwarta |
"Abin da na gani shine muna zaune sai ta fara tari, sai ta rike ni kwarai ta ce mani ina jin bana da lafiya, nima na rike ta sosai, sai ta ce waiyo! waiyo!! har sau biyu, sai na ce Inna lillahi wa'inna ilehi raji'un na sake maimaitawa, sai ta karba ta ce Inna lillahi wa'inna ilehi raji'un , Allah ya bata ikon fadin haka, sai na ce La ila ha illallah Muhammadu rasurullahi sallallahu alaihi wasallam, ita ma Allah ya bata ikon fadin haka, duk abin da na fada shi ne ta maimaita.
"Daga nan sai sarin jini da gudajensa ya dinga fitowa daga bakinta, sai wani bawan Allah ya zo ya taimaka mana aka kaita gefe aka kwantar da ita, daga nan Allah ya yi mata cikawa, bakin abin da na sani kenan"
Wata tsohuwa cikin alhini bayan rasuwar Aisha |
Mujallar ISYAKU.COM da duk ma'aikatanta, muna yi wa Mama Aisha addu'ar Allah ya karbi bakoncin ta ya sa ta cikin rahamarsa, ya sanyaya mata, ya yafe mata kura-kurenta, ya saka ta a Aljannah Firdaus. Mama Aisha ta sami kyakkyawan karshe, Allah ya sa mu cika da imani idan tamu ta zo. Amin.
DAGA ISYAKU.COM Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp