Rundunar yansandan jihar Kebbi ta kama masu ba masu sace mutane bayan sirri guda arba'in da shida 46, ta kuma dakile wani yunkurin sace wani mutum domin a karbi fansar Naira Miliyan daya da rabi N1.5m daga wajensa. Kwamishinan yansandan jihar Kebbi Mr. Garba M. Danjuma ne ya shaida wa manema labarai haka a shelkwatan yansanda da ke Birnin kebbi.
Kwamishinan ya ce wani mutum main suna Alhaji Abubakar Chindo wanda ke garin Bunza, a karamar hukumar Bunza ya shaida wa yansanda cewa an kira shi a wayar salula aka bukaci ya biya Naira miliyan daya da rabi ko a sace shi
"Sakamako haka jami'an mu masu bincike suka fara aiki.,wanda ya kai ga kama Muhammed da Abdullahi bisa zargin alaka da wannan yunkuri" inji Kwamishinan yansanda .
Ya kuma kara da cewa rundunarsa ta yi nassarar kama wasu da ake zargi da harkar sace mutane a kananan hukumomin Fakai, Arewa,Danko-Wasagu, Jega, Birnin kebbi, Shanga,, Bunza da Zuru.
Rundunar yansandan ta kuma kama da dama daga cikin masu bayar da bayanan sirri ga masu sace mutane daga karamar hukumar Gwandu , hakazalika ta kama wani mai suna Labbo daga kauyen Ingarje a karamar hukumar Jega, wanda ya ke cikin wani gungun masu sace mutane da suka sace matar Saidu Abdullahi a wannan yanki.
Kwamishina Danjuma ya ce rundunarsa za ta gurfanar da su a gaban Kotu.
.DAGA ISYAKU.COM Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp
Kwamishinan ya ce wani mutum main suna Alhaji Abubakar Chindo wanda ke garin Bunza, a karamar hukumar Bunza ya shaida wa yansanda cewa an kira shi a wayar salula aka bukaci ya biya Naira miliyan daya da rabi ko a sace shi
"Sakamako haka jami'an mu masu bincike suka fara aiki.,wanda ya kai ga kama Muhammed da Abdullahi bisa zargin alaka da wannan yunkuri" inji Kwamishinan yansanda .
Ya kuma kara da cewa rundunarsa ta yi nassarar kama wasu da ake zargi da harkar sace mutane a kananan hukumomin Fakai, Arewa,Danko-Wasagu, Jega, Birnin kebbi, Shanga,, Bunza da Zuru.
Rundunar yansandan ta kuma kama da dama daga cikin masu bayar da bayanan sirri ga masu sace mutane daga karamar hukumar Gwandu , hakazalika ta kama wani mai suna Labbo daga kauyen Ingarje a karamar hukumar Jega, wanda ya ke cikin wani gungun masu sace mutane da suka sace matar Saidu Abdullahi a wannan yanki.
Kwamishina Danjuma ya ce rundunarsa za ta gurfanar da su a gaban Kotu.
.DAGA ISYAKU.COM Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp