Legit Hausa
Bayan bayyanar tonon sililin da ake yiwa malaman jami'a akan
lalata da suke yi da dalibai su ba su maki, wata budurwa mai suna Busayo ta
bayyana yadda tayi fama da wani dan iskan malamin jami'a.
A cewar ta Lakcaran wanda ta bayyana sunansa da Dr. Abdul ya
fadar da ita jarrabawar shi saboda ta ki yarda ta yi lalata da shi.
Budurwar ta kuma wallafa hotunan hirar da suka yi da shi a
manhajar WhatsApp domin tabbatar da faruwar lamarin.
A hotunan da ta wallafa na hirar ta su a WhatsApp din,
malamin yana ta faman rokon ta gafara amma ita kuma ta yi kunnen uwar shegu da
shi.
A hirar ta su Busayo ta yi ta zagin Lakcaran, hakan na nuni
da cewa har yanzu ta na jin haushin irin abinda Dr. Abdul ya yi mata. Ga dai
hotunan da Busayo ta wallafa na hirar da suka yi da Malamin Jami'ar a kasa:
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp