Legit Hausa
Kwamitin da gwamnatin jihar Zamfara ta kafa don shawo kan
matsalar tsaron jihar ta bada shawarar sauke sarakuna 5 da dagatai 33 a rahoton
da suka mika ranar juma'a. Yayin mika rahoton ga gwamna Muhammad Bello
Matawalle, shugaban kwamitin, Alhaji M.D Abubakar, tsohon sifetan 'yan sanda
mai murabus, ya ce sarakunan 5, dagatai 33 da wasu masu anguwanni a jihar na da
sa hannu a tabarbarewar tsaron jihar.
Tsohon sifetan 'yan sandan ya ce, "Kwamitin na bada
shawarar sauke sarakuna 5, dagatai 33 da kuma masu anguwannin da ke da sa hannu
a matsalar tsaron." Kamar yadda kwamitin ya sanar, daga rahoton da suka
samu, za a gurfanar da daya daga cikin sarakunan a kotu saboda zarginsa da ake
da taimakawa kashe-kashe da boye 'yan ta'addan.
Kwamitin ya kuma bada shawarar gyara ga yanayin mulkin duk
masarautu 17 da ke jihar don tsaftace yanayin sarautar gargajiyar jihar.
Kwamitin ya kara da bawa gwamnatin tarayya shawarar gurfanar da sojoji goma a
kotun sojin Najeriya akan hannunsu tsundum da ta kama a mummunan aikin a jihar.
Kwamitin ta kara da shawartar hukumar 'yan sanda da ta kori
jami'anta 4, wasu hudun kuma ta rage musu matsayi sai kuma 7 ta kara musu
girma. Shugaban kwamitin ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta tabbatar da
shawarwarin kwamitin don kuwa zaman lafiyar jihar ya dogara ne a kokarin
gwamnan na cire banbancin siyasa yayin zartar da hukunci.
A maida martaninsa, gwamna matawalle ya jinjinawa kwamitin
akan aikin da suka yi. Ya kuma tabbatar musu da cewa, rantsuwarsa ta kare
hakkoki da rayuwar mutanen jihar duk da banbancin siyasa, kabila ko addini
bazata tashi a banza ba.
Ya kara da cewa, zai gana da shugaban kasa akan shawarwarin
da suka danganci gwamnatin tarayya. Duk da kuwa kwamitin bai sanar da sarakunan
da abun ya shafa ba yayin mika rahoton, wasu daga cikin sarakunan basa wajen.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp