Pantami ya taka wa MTN birki bayan sun bullo da sabon tsarin sakuce wa jama'a kudi

Legit Hausa
Ma'aikatar sadarwa ta tarayya ta ce an ja hankalinta a kan wani sako da kamfanin sadarwa na MTN ke tura wa kwastomominsa a kan cewa zai fara cire naira hudu (N4:00) daga asusun duk wanda ya sayi katin waya na kamfanin daga asusunsa na banki.
Jama'a sun wayi gari da samun sako a wayoyinsu na hannu a kan wannan sabon tsari da kamfanin sadarwa na MTN ke shirin fara aiki da shi daga ranar Litinin, 21 ga watan Oktoba, 2019.
Ofishin minstan sadarwa, Dakta Isa Ali Pantami, ne ya ankarar da ma'aikatar sadarwa a kan wannan sabon tsari da MTN ke shirin kaddamar wa bayan jama'a sun mika kukansu gare shi a dandalin sada zumunta na Tuwita a ranar Lahadi.
Pantami ya ce bashi da masaniya a kan sabon tsarin da kamfanin sadarwa na MTN ya bullo da shi, a saboda haka ne ya umarci hukumar kula da kamfanonin sadarwa da ke Najeriya (NCC) da ta tabbatar cewa MTN ta dakatar da wannan sabon tsari da ta bullo da shi kuma take shirin kaddamar wa a ranar Litinin.
Da yake jinjina wa Pantami a kan daukan mataki a kan lokaci, Joe Abba, tsohon hadimi a gwamnatin Buhari, ya ce yanzu haka kamfanin sadarwa na MTN ya dakatar da sabon tsarin sakamakon umarnin da Pantami ya bayar.
Jama'a na yawan korafi a kan yadda kamfanonin sadar wa a Najeriya ke bullo da tsare-tsare masu suna daban-daban domin raba su da 'yan sulallansu na yin kira a waya.
DAGA ISYAKU.COM Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN