Legit Hausa
Sabanin rahotanni daga wasu kafofin watsa labarai na kasar
nan suka yada dangane da cewa an samu nasarar cafke zakin da ya tsere daga
gidan adana namun daji na jihar Kano, mahukuntan gidan sun yi karin haske.
Mahukanta a gidan adana namun dajin Kano sun ce ya zuwa yanzu ba a kai ga kama
zakin da ya kufce ba daga wurin da aka killace shi.
Da yake ganawa da manema labarai na jaridar Kano Focus
dangane da tserewar zakin, shugaban gidan adana namun dajin, Alhaji Saidu
Gwadabe, ya ce tuni aka baza kwararru a fannin kama zakuna domin lalubo inda ya
buya tare da mayar da shi wurin killatarsa.
A cewar Gwadabe, ko kadan batun da wasu kafofin watsa
labarai suka yada dangane da kama zakin ba gaskiya bane, domin kuwa ya zuwa
yanzu harbin da aka yi wa Zakin har sau biyu da harsashi mai sanya bacci bai yi
tasiri ba inda ko gizau bai yi ba, sai dai ya nemi al’umma da su kwantar da
hankulansu.
Dangane da irin
ta'asar da Zakin ya tafka bayan kufcewarsa, ya yi wa akuyoyi jina-jina biyon
bayan afkawa garkensu da ya yi wanda harabar ma'adanar namun dajin.
Sai kuma jimina guda a wadda har yanzu an turke shi a
kejinta. Ko a shekarun baya dai gidan adana namun dajin na jihar Kano ya
fuskanci tserewar Kadaji wanda lamarin makamancin wannan ya haddasa tsoro a
zukatan al'umma musamman wadanda ke makotaka da gidan adana namun dawan.
DAGA ISYAKU.COM Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp https://chat.whatsapp.com/Hp4xUtixUxh5d76Kw2TGpp
Tags:
LABARI