Legit Hausa
Kotun zaben yan majalisar dattawa dake Ado-Ekiti, birnin
jihar Ekiti ta soke nasarar kakakin majalisar dattawa, Sanata Dayo Adeyeye, na
jam'iyyar All Progressives Congress APC, a zaben 23 ga Febrairu, 2019. Bayan
soke nasararsa, kotun ta alanta abokiyar hamayyarsa ta jam'iyyar Peoples
Democratic Party PDP, Sanata Biodun Olujimi, matsayin wacce ta lashe zaben na
halas.
A watan Febrairu, hukumar gudanar da zabe ta kasa mai zaman
kanta INEC ta alanta Adeyeye a matsayin wanda ya lashe zaben. Hakan ya sa Bidun
Adeyeye ta garzaya kotu domin kwato hakkinta. Ta bayyanawa kotu cewa ita ta
samu rinjayen kuri'u amma INEC danne mata hakkinta.
Olujimi ta bukaci kotun ta soke nasarar abokin hamayyarta,
Dayo Adeyeye, kuma a gudanar da sabon zabe. Yayinda ake yanke hukuncin,
kwamitin alkalan karkashin jagorancin, Alkali D.D Adeck, ya soke zaben wasu
yankunan mazabar kuma ya alanta Biodun Olujimi ta PDP matsayin wacce ta lashe
zaben. A karshe, kotu ta ce Olujimi ta samu kuri'u 54,894, yayinda Sanata Dayo
Adeyey ya samu kuri'u 52,243.
A wani labarin mai kama da haka, Jam'iyyar APC ta ce zata
daukaka kara akan nasarar tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawa da kotu
ta tabbatar. Shugaban jam'iyyar APC na jihar Enugu, Ben Nwoye, a tattaunawar da
yayi da kamfanin dillancin labarai akan hukuncin da kotun sauraron kararrakin
zabe ta yanke ne ya tabbatar da hakan.
'Yar takarar kujerar sanata ta yankin yammacin Enugu, Juliet
Ibekaku-Nwaguwu ta jam'iyyar APC ta tunkari kotun sauraron kararrakin zaben da
korafi bayan an bayyana Ekwerwmadu a matsayin wanda ya lashe zaben.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN