Legit Hausa
Majalisar kasar Iran ta sanya hannu akan wata doka da zata
kare hakkin yara kanana ciki kuwa hadda baiwa wani mutumi damar auren 'yarsa da
ya dauko riko duk kuwa da cewa shekarunta 13 a duniya.
Sai dai kuma kungiyoyin kare hakkin dan adam na kasar sun yo
caa akan wannan doka da majalisar kasar ta sanyawa hannu, wacce zata dinga
baiwwa iyaye maza damar auren 'ya'yansu mata da suka dauko riko.
Manyan kasar ta Iran, sun duba wannan doka da majalisar ta
aika musu sun kuma kwatanta ta da hallacinta a addinin musulunci, amma har
yanzu ba ta gabatar da hukunci a kai ba. A kasar Iran yarinya 'yar shekara 13
za ta iya aure amma idan alkali ya bayar da dama. Zuwa yanzu dai auren 'ya'yan
riko bai hallata ba a kasar.
Yara mata 42,000 ne wadanda suke tsakanin shekara 10 zuwa 14
suka yi aure a shekarar 2010, kamar yadda shafin yanar gizo na Tabnak ya
wallafa.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN