Legit Hausa
Matamakin Shugaban kasa Yemi Osinbajo yace zai jingine
kariyar da kundin tsarin mulki ta bashi domin a bincike shi. “A yan kwanakin da
suka gabata, wasu bayanan karya na ta yawo a kafofin watsa labarai akaina,
wanda wata kungiyar mahasadda ke ta kitsawa,” ya wallafa a shafin twitter.
“Labarin na bata da suna da batarwar da wannan kungiya ta
shirya na ta yawo kafofin sadarwa ba tare da suna ba. “A yau na bayar da
umurnin fara daukar mataki na doka akan wasu mutane biyu, daya Timi Frank da
kuma wani Katch Ononuju, wadanda suka sanya sunayensu akan labaran karyan.
“Zan jingine kariyar da kundin tsarin mulku ta bani domin ba
kotu damar hukunci akan wannan iikirari na batanci da karya," inji
Osinbajo. Timi Frank, tsohon mataimakin sakataren labaran jam’iyyar All Progressives
Congress (APC), yayi zargin cewa hukumar tattara kudaden shiga na tarayya
(FIRS) ta bayar da naira biliyan 900 ga mataimakin Shugaban kasa don kamfen din
zabe, zargin da tuni hukumar harajin ta karyata. Amma tuni Frank yayi martani
inda ya bukaci hukumar FIRS ta daina yaudarar yan Najeriya.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN