Legit Hausa
Kotun sauraron kararrakin zabe na majalisar dokokin jiha da
ke zama a Sokoto, a ranar Laraba, 25 ga watan Satumba, ta jaddada zaben
mambobin majalisar dokokin jihar Sokoto, da ke wakiltan mazabar Gada ta yamma,
Hon. Kabiru Dauda da mai wakiltan mazabar Rabah, Hon. Abubakar Zakari.
Dan takarar jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a zaben
ranar 9 ga watan Maris, 2019, a mazabar Gada ta yamma, Hon. Garba Yakubu Tsitse
ne ya kalubalanci kaddamar da Dauda na jam’iyyar All Progressives Congress (
APC) a matsayin wanda ya lashe zaben.
Hakazalika, dan takarar jam’iyyar Peoples Democratic Party
(PDP), a zaben mazabar Rabah, Hon. Abubakar Gandi ya kalubalanci kaddamar da
Zakari na APC a matsayin wanda ya lashe zaben.
A kararrakinsu, yan takarar sun yi zargin cewa wadanda ake
karan basu samu mafi yawan kuri’un da aka kada bisa doka ba, sannan cewa zaben
bai gudana daidai da dokar zabe na 2010 ba, da kuma tsarin jadawalin INEC na
zaben 2019 ba.
Da yake yanke hukunci, Shugaban kotun zaben, Justis Ubale
Yusuf, yace dukkanin kararrakin basu da inganci. Yayi bayanin cewa masu karar
sun gaza tabbatar da shari’arsu. Don haka Justis Yusuf yayi watsi da
kararrakin.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN