Dusashewar karfin mazakuta: 'Yan sanda sun fara binciken wani mutum da laifin 'shafi mulera'

Legit Hausa
Rundunar 'yan sandan Najeriya reshen jihar Enugu sun fara binciken korafin da wani mutum, Mista Sunday, ya shigar a gabanta bisa dusashewar karfin mazakutarsa bayan ya gaisa da wani gurgu mai suna Anayo.
SP Ebere Amaraizu, kakakin rundunar 'yan sandan jihar Enugu, ya tabbatar da faruwar hakan ga kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) a ranar Lahadi.
Amaraizu ya ce lamarin ya faru ne ranar 13 ga watan Satumba a yankin kwanar Obiagu da ke unguwar Ogui a cikin birnin Enugu.
Kakakin rundunar 'yan sandan ya ce wanda ake zargi da aikata laifin 'shafi mulera' yana da nakasa (bukata ta musamman)
"Hedikwatar 'yan sanda na gudanar da bincike ta hannun ofishinta da ke unguwar Ogui domin warware rudanin da ke tattare da korafin da wani mutum ya shigar a kan dusashewar karfin mazakutarsa jim kadan bayan ya gaisa da wani mutum a Enugu.
"Mutumin mai suna Sunday ya ankarar da jama'a abin da ya faru kuma ya nuna mutumin da yake zargi da daukewar karfin mazakutarsa bayan sun gaisa.
"Yana zargin wani mai suna Anayo da dusashewar karfin mazakutarsa, lamarin da yasa jama'a suka lakada masa shegen duka kafin daga bisani jami'an 'yan sanda daga ofishin Ogui su kwace shi da kyar," a cewarsa.
Amaraizu ya ce rundunar 'yan sanda na gudanar da bincike a kan lamarin.
DAGA ISYAKU.COM Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN