Legit Hausa
Wani dan kungiyar Boko Haram da ya tuba ya bayyana yadda
shugabannin kungiyar suka yaudare shi da sunan jihadi aka suka jefa shi cikin
bala'i da masifa. Idan ba a manta ba kungiyar dai ta jawo hankalin matasa da
yawa a kasar nan, inda suka dinga rububin shiga cikinta, yayin da kuma wasu
wanda basu da ra'ayin shiga ta tilasta su ta dole bayan ta sace su, sannan ta
dinga yi musu barazanar kisa idan har suka sake suka fita daga cikinta.
Wani matashi tsohon dan kungiyar wanda ya tuba yanzu ya
bayyana cewa rashin aikin yine ya jefa shi cikin wannan harkar. "Sun
yaudare mu ne ta hanyar yi mana da'awa da addinin Musulunci, sai da muka duba
muka gani cewa ashe ba Musulunci ba ne," a cewar matashin da ya tuba daga
harkar kamar yadda ya bayyanawa jaridar BBC.
Saurayin ya bayyana cewa a lokacin kafin su shiga kungiyar,
suna ganin wani abokinsu yana zuwa da kudi, yayin da su kuma suke ta kokarin
ganin yadda zasu yi su samu kudin sun asa. Ya cigaba da cewa abokin nasu ya ja
wasu daga cikinsu, inda da farko ake biyansu naira dubu uku a duk lokacin da
suka kai hari, ko kuma suka kwato kudi ko kuma aka biyasu kudin fansa.
Ya ce a lokacin abin da ake ba su bai wuce Naira 3,000 ba,
kuma za a ce akwai manya wadanda za su zo su ba su Naira dubu 500 ko dubu 600.
Matashin wanda ya shafe shekara takwas tare da Boko Haram, ya ce da farko yana
jin dadin cewa addinin Musulunci yake yi wa aiki. Amma daga baya da ya gano
cewa kungiyar ta kauce wa addinin Musulunci ya shiga damuwa sosai.
“Ga Kur’ani a ajiye, na duba na ga Allah Ya hana zina, ya
hana shaye-shaye, sai na ga cewa ga kwayoyin, ga zinar, a kamo mata a zo a yi
ta zina da su, wani ma bai damu da Sallah ba kuma za a zo a kashe wanda yake
Sallar,” inji shi. Daga karshe matashin tare da wadansu takwarorinsa 20 sun
yanke shawarar barin kungiyar, bayan da suka gaji da kuncin rayuwa da suke
fuskanta.
Sannan suka mika kansu ga sojojin Najeriya, inda daga baya
aka koyar da su sana’o’i. A yanzu matashin ya koyi sana’ar kafinta, kuma ya ce
rayuwarsa ta inganta, domin yana yin aiki ana biyansa, kuma yana samun karbuwa
a sana’ar ta sa.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi