Legit Hausa
'Yan uwa da
abokan arzikin wani manaja banki da aka bayyana sunansa da Ibeakanma Onyechere
sun shiga halin dimuwa da juyayi bayan samun kabarin cewa ya kashe kansa a
unguwar Victoria Island, a jihar Legas.
Onyechere, manajan hulda da jama'a a daya daga cikin
fitattun bankunan kasar nan, ya kashe kansa ta hanyar kwankwadar maganin kwarin
nan mai karfi 'Sniper' a cikin makon jiya.
Ana zargin cewa manajan bankin ya kashe kansa ne biyo bayan
matsananciyar damuwa, musamman irin kalaman da ya wallafa a shafinsa na sada
zumunta 'Facebook da Twitter' a ranar 24 ga watan Yuli, inda ya rubuta cikin
harshen turanci cewa, "sannu a hankali hasken sai dusashe wa yake
yi."
A wasiyyar da ya bari a cikin wata wasika da ya rubuta kafin
mutuwarsa, Onyechere ya bayyana irin soyayyarsa ga matarsa, Cecilia, da kuma
diyarsu tare da rokon cewa kar matarsa ta yi kuka saboda mutuwarsa. DUBA
WANNAN: Boko Haram: An yi bikin Sallah a Bama a karo na farko cikin shekaru
biyar "Ina kiran ki da 'sahibata', saboda kaunar da nake yi maki. Ina so
ki sani cewa karshen rayuwata a duniya ya zo.
Abinda ke damuna ya samu galaba a kai na, ya kuma kawo
karshen dukkan wata damu wa ta. Kin yi kuskuren aure na, kin cancanci miji na
arziki, ba iri na ba. Kina bukatar farin ciki na gaskiya, kar ki yi kuka saboda
mutuwa ta. "Ki sanar da diyar mu, Chinenyenwa, cewa ina son ta sosai.
Ki zauna lafiya da kowa, duk da na san haka abu ne mai wuya.
Ki sanar da dangi na cewa ina rokonsu kar wanda ya tsangwame ki bayan mutuwa
ta. Kar ki min kuka, addu'arki nake bukata. Sai wata rana masoyiya ta,"
kamar yadda ya rubuta cikin wasikar.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi