Shugaba Buhari ya karbi bakuncin gwamnoni da manyan yan APC a Daura (hotuna)


Legit Hausa

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karbi bakuncin gwamnonin APC da sauran manyan masu ruwa da tsaki a Daura, jihar Katsina a ranar Talata, 13 ga watan Agusta. Manyan jiga-jigan jam’iyyar mai mulki sun kai wa Shugaban kasar gaisuwar babban sallah ne a gidansa da ke mahaifarsa na Daura.

Gwamnonin a suka hallara sun hada da na jihar Katsina, Aminu Bello Masar; gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi; gwamnan jihar Lagas, Babajide Sanwo Olu; gwamnan jihar Kebbi, Atiku Bagudu; gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai da kuma gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki Sauran manyan masu ruwa da tsakin da suka hallara sun hada da Shugaban kamfanin man fetur na Najeriya (NNPC), Mele Kyari; Shugaban NITDA, Isa Ali Pantami da kuma mukaddashin Shugaban EFCC, Ibrahim Magu, da dai sauransu.
 

DAGA ISYAKU.COM

Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN