Legit Hausa
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya karbi bakuncin gwamnonin
APC da sauran manyan masu ruwa da tsaki a Daura, jihar Katsina a ranar Talata,
13 ga watan Agusta. Manyan jiga-jigan jam’iyyar mai mulki sun kai wa Shugaban
kasar gaisuwar babban sallah ne a gidansa da ke mahaifarsa na Daura.
Gwamnonin a suka hallara sun hada da na jihar Katsina, Aminu
Bello Masar; gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi; gwamnan jihar Lagas, Babajide
Sanwo Olu; gwamnan jihar Kebbi, Atiku Bagudu; gwamnan jihar Kaduna, Nasir
El-Rufai da kuma gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki Sauran manyan masu ruwa da
tsakin da suka hallara sun hada da Shugaban kamfanin man fetur na Najeriya
(NNPC), Mele Kyari; Shugaban NITDA, Isa Ali Pantami da kuma mukaddashin
Shugaban EFCC, Ibrahim Magu, da dai sauransu.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi