Legit Hausa
Komai ya kankama domin tafiyar shugaban kungiyar IMN wanda
akafi sani da Shi'a, SheikIbrahim El-Zakzaky, kasar Indiya domin jinya biyo
bayan belin da kotun jihar Kaduna ta bashi a makon da ya gabata. Mun kawo muku
rahoton cewa an tafi da Sheik Ibrahim Zakzaky birnin tarayya Abuja.
El-Zakzaky zai tafi Indiya tare da matarsa Zeenat inda za su
nufi Asibitin Medenta dake New Delhi a kasar ta Indiya domin a duba lafiyarsu.
Wata majiyar IMN dake Kaduna ce ta sanar da wakilin Daily Trust wannan labarin
inda ta ce, jagoran na IMN yanzu haka yana Abuja tare da jami’an tsaron DSS
inda yake jiran tashinsu zuwa Indiya a wani karamin jirgin sama.
A yanzu haka, Sheikh Zakzaky da iyalinsa suna babban filin
jirgin saman Nnamdi Azikwe dake Abuja kuma zasu tashi da jirgin Emirates
misalin karfe 6 daidai.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi