Legit Hausa
A sakamakon yunkuri da gwamnatin tarayya ke yin a hana shigo
da shinkafa yar kasar waje, kungiyar manoman shinkafar Najeriya ta ce, daga
yanzu farashin buhun shinkafa ba zai haura 15,000 ba.
Shugaban kungiyar na kasa, Alhaji Mohammed Abubakar Maifata,
a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar Alhamis, 29 ga watan Agusta
a Abuja, ya bayyana cewa kungiyar za ta dauki mataki akan duk wanda aka samu
yana sayar da buhun shinkafa sama da farashin kungiya.
A cewar Maifata, shinkafa yar gida da ake yi a Niaeriya ba
ta wuce tsakanin naira 13,300 zuwa 14,000, yayin da ita kuma ta gwamnati ta kai
15,000. Kungiyar ta bayyana cewa, ta aike wa gwamnatin tarayya wasika akan
karya farashin shinkafa, domin ta karfafa mata wajen hana fasakaurin shinkafa a
kasar nan.
Shuwagabannin kungiyar RIPAN sun bayyana cewa, Najeriya na
asarar dala miliyan 400 wajen fasakaurin shinkafa daga kasar Jamhuriyar Benin.
Har ila yau Maifata tare da mataimakinsa Mista Paul Eluhaiwe sun bayyana cewa,
sun kammala tuntubar mutanensu da ke bakin iyakar kasar.
Shugaban RIPAN din ya ci gaba da cewa, akwai tan 500,000 na
shinkafa da ake kan hanyar shigo da su kasar nan daga Thailand kafin bikin
kirsimeti. A cewar shi, ba shakka wannan zai sa masu fasakaurin shinkafa su yi
asarar dala miliyan 4000.
A bangaransa, rufe iyakar da ke tsakanin Najeriya da kasar
Benin zai taimaka wajen dakile fasakaurin shinkafa tare habbaka shinkafar gida.
Ya kara da cewa, kungiyar tana goyan bayan gwamnatin tarayya wajen kulle iyakar
kasar nan.
Kungiyar ta babbatar wa ‘yan Najeriya cewa, za ta saka wa
‘ya’yan kungiyar haraji domin ta cike gurbin farashin shinkafa a kasuwa,
sakamakon rufe iyakar kasar. Ta kara da cewa, kasar nan tana bukatar tan
miliyan hudu na shinkafa a duk sheka, amma mambobin kungiyar za su shigo da
shinkafa wanda ya kai tan miliyan biyar.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa Shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN