Legit Hausa
Rahotanni sun kawo cewa akalla mutane biyar ne suka mutu
yayinda aka kona wasu gidaje da dama, a wani hari da wasu yan bindiga suka kai
kauyen Zangan da ke Takad a karamar hukumar Kaura da ke jihar Kaduna.
Mista Bege Katuka, Shugaban rikon kwarya na karamar hukumar
wanda ya tabbatar da lamarin ga manema labarai a ranar Juma’a, 30 ga watan
Agusta, yace maharan sun kai mamaya kauyen da misalin karfe 4:00 na yammacin
ranar Alhamis, sannan suka yi ta harbi ba kakkautawa akan bayin Allah.
“An kashe mutane
biyar yayinda har yanzu ba a ga wasu biyu ba. An kuma kona wasu gidaje da dama.
“Mun bukaci mutane da su kwantar da hankalinsu sannan su yi imani da jami’an
tsaro da suka riga suka yi wa yankin kawanya yayinda ake ci gaba da gudanar da
bincike,” inji shi.
Jaridar Daily Trust cewa kauyen Zangan inda mummunan
al’amarin ya afku, na raba iyaka da karamar hukumar Riyom da ke jihar Plateau.
A halin da ake ciki, duk wani kokari da ake don tabbatar da lamarin daga
kakakin yan sandan jihar, DSP Yakubu Sabo ya ci tura domin bai amsa kiran waya
da sakon da aka tura masa ba.
DAGA ISYAKU.COM
Latsa Shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp
https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN