Legit Hausa
Yan sa’o’i kadan bayan sanar dashi a matsayin daya daga
cikin zababbun ministocin shugaban kasa Muhammadu Buhari, dan majalisar
wakilai, Emeka Nwajiuba, ya sanar da sauya shekarsa daga jam’iyyar Accord Party
zuwa jam’iyyar All Progressives Congress (APC).
Jawabin sauya shekar Nwajiuba na kunshe ne a cikin wata
wasika da mataimakin kakakin majalisar wakilai, Ahmed Idris Wasu ya karanto a
zauren majalisa. Dan majalisar na jihar Imo, wanda ya samu siga majalisar
wakilai ta tara a karkashin inuwar jam’iyyar Accord Party, ya ci moriyar
hukuncin kotu ne da ta tsige Chike Okafor na APC.
Kotu ta bayyana cewa jam'iyyar APC bata bi ka'idoji wajen
zabar Okafor ba. kafin sauya shekarsa zuwa Accord, Nwajiuba, wanda ke wakiltan
mazabar Ehime Mbano/Ihite Uboma/Obowo na jihar Imo, ya kasance dan APC.
Kasancewarsa dan kashenin Buhari, bai zamo abun mamaki ba a lokacin da sunan
Nwajiuba ya bayyana a cikin jerin sunayen ministoci 43 da aka gabatarwa
majalisa duk da kasancewarsa dan jam;’iyyar adawa.
A wani labari makamancin haka, Legit.ng ta rahoto cewa
tsohon Gwamnan Akwa Ibom, Godswill Akpabio wanda sunansa ke cikin jerin sunayen
sabbin ministocin da Buhari ya aikawa majalisa, ya ce zai yi iya bakin
kokarinsa a duk ma’aikatar da Shugaban kasa ya damka masa. Akpabio ya fadi wannan
maganar ne yayin hirarsa da manema labarai jim kadan bayan majaliasar dattawa
ta kammala tantance shi a ranar Laraba.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi