Legit Hausa
Simeon Achuba, mataimakin gwamnan jihar Kogi ya yi ikirarin
cewa zai kai karar Gwamna Yahaya Bello zuwa kotu bisa rashin biyansa albashi
tun na shekarar 2017, kudin da jimillarsu ta kama N819m. Achuba wanda ya
kasance mataimakin gwamnan na Kogi tsawon shekaru biyu kenan yanzu, ya rubuta
ma gwamnan wasika ta hanyar lauyansa Cif Femi Falana ( SAN).
A cikin wasikar ya nemi Gwamna Bello ya biya shi hakkinsa
cikin mako guda kacal. A yau Laraba 24 ga watan Yulin 2019 ne wa’adin mako
gudan da mataimakin gwamnan ya bada ke cika. Manema labarai na cigaba da zuba
ido domin ganin abinda zai biyo bayan cikar wa’adin na mako guda. Idan baku
manta ba, a kwanakin baya, ma’aikatan jihar Kogi sun bayyana bacin ransu
sakamakon rashin biyansu albashin da gwamnan jahar bai yi.
Wannan al’amari yayi kamari kwarai da gaske saboda ba wai
ma’aikata kadai suka koka da lamarin ba hadda masu karbar fansho. A cewar da
dama daga cikinsu, “ Muna cikin tsaka mai wuya, mun rasa inda zamu sa kanmu.”
Haka zalika, lamarin rashin biyan albashin ya fusata
Kungiyar Malamai ta kasa wato NUT, inda shugaban kungiyar reshen jihar Kogi,
Thomas Ayodele ya ce, malaman makaranta ne ya kamata a ce sune kan gaba wurin
karbar albashi amma sai gashi abin takaici anyi biris da al’amarinmu.
Wani malamin makarantar firamare, Audu Austin ya bamu
labarin cewa, ana dadewa ba a biya albashin ba kuma idan ma an tashi biya ba
cikakken albashin ake badawa ba.
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi