Legit Hausa
A kwanakin baya an yi ta yada jita-jitar Shugaban Kasa
Muhammadu Buhari zai mika sunan fitaccen dan wasan Hausa na Kannywood Ali Nuhu
Mohammed a matsayin Ministan matasa da wasanni. Sai dai kuma a sunayen shugaban
kasar ya bayar domin a tantancewa su babu sunan Ali Nuhu a ciki.
Wannan lamari ya janyo kace-nace a kafafen sada zumunta.
Sardaunan Matasan Rijiyar Lemo dake jihar Kano cewa yayi: "Wai shi Ali
Nuhu da ake cewa za a bashi kujerar Minista a karkashin wace jiha zai tashi?
Kano, Gombe ko kuma Plataeu?"
Haka shi kuma wani shafin Hausa na Facebook
mai suna Hausa7 sun sanya hoton Ali Nuhu ne yana fada da wani (kuma akwai
yiwuwar an dauki wurin a cikin fim ne) amma sai suka ce daga majiya mai tushe
sun jiyo cewa ya fara fada da abokanan aikinsa wanda yake tunanin sune suka yi
masa kafar ungulu.
Haka ita ma wata mai amfani da shafin sada zumunta na
Facebook mai suna Husnah Ahmad ta sanya hotunan gwamnan jihar Kano Abdullahi
Umar Ganduje da shugaban jam'iyyar jihar Kano na APC, Abdullahi Abbas da kuma
Ali Nuhu, inda a karshe tayi wani rubutu na hirar barkwanci kamar haka:
Ali Nuhu: Gwamna ban ji sunana ba cikin ministocin nan?
Ganduje: To kai banda abinka nima ba a saka sunan wadanda na
bayar ba.
Ali Nuhu: Au dama baka sanya sunana ba kenan?
Ganduje: Na manta ne.
Audu Ciranci: To kai Ali Nuhu ai nima ba a saka sunana ba!
Ali Nuhu: To ai kai bakada ilimi
DAGA ISYAKU.COM
Shiga shafinmu na Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/D9SKfH2BjM4Deldar0KkFN
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi