Zargin aringizon kuri'u: Kotu ta amince da bukatar PDP na binciken kayayyakin zaben Kano


Legit Hausa

Kotun da ke sauraron korafe korafe kan zaben gwamnan jihar Kano ta amince da bukatar jam'iyyar PDP na binciken kayayyakin da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta yi amfani da su wajen gudanar da zaben gwamnan jihar.

Dan takarar gwamnan jihar karkashin jam'iyyar PDP Alhaji Abba Kabiru Yusuf na kalubalantar nasarar da hukumar zaben ta ce gwamna Abdullahi Ganduje na jam'iyyar APC ya samu a zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 23 ga watan Maris.

A cikin wata takardar korafi da ya gabatar gaban kotun, wacce ke karkashin mai shari'a Halima Shamaki, lauyan dan takarar PDP, Maliki Kuliya-Umar ya bukacin kotun da ta umurci INEC ta baiwa jam'iyyar kayayyakin da aka gudanar da zaben da su a ranar 9 ga watan Maris da kuma 23 ga watan Maris domin ta yi bincike kan su.

Mai shari'a Shamaki ta umurci INEC da ta baiwa jam'iyyar dukkanin kayayyakin zaben da ta yi amfani da su wajen gudanar da zaben Kano, bisa ga dalilan da jam'iyyar ta bayar na son binciken kayayyakin. Kamfanin dillancin labarai na kasa NAN ya ruwaito cewa jam'iyyar PDP na da kwanaki biyar ta shigar da APC kara kotu bayan da ta cinye kwanaki 15 cikin 21 da dokar zaben kasar ta 2010 ta tanar kamar yadda aka sabunta.


DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN