Type Here to Get Search Results !

Gwamnatin jihar Kebbi bata saukar da Kwamishinoninta ba

Gwamnatin jihar Kebbi bata saukar da Kwamishinoninta ba kamar yadda ake yadawa a shafukan sada zumunta. Wannan ya biyo bayan jita jita da wasu ma'abuta amfani da kafofin sada zumunta ke yadawa a shafukansu yan kwanaki da suka gabata a jihar Kebbi.

Wata majiya kwakkwara ta shaida mana cewa ba haka zancen yake ba. Majiyarmu ta ce wata takarda ce Gwamnatin jihar Kebbi ta rubuta zuwa ga Sakataren Gwamnatin jihar Kebbi inda ta bukaci ya aika takardun ga Kwamishinoni, kuma ana bukatar su rubuto wa Gwamnati rahotun ma'aikatarsu yadda lamaurra suka kasance daga 2015 zuwa 2019 tare da bayani inda ake da matsaloli a ma'aikatunsu da shawara yadda za'a magance su.

Wannan salon al'ada ce ga kowane zangon mulki a matakai na shugabanci matukar mulki ya zo karshe, kafin a saukar da zubin jerin shugabannin ma'aikatu.

Hakazalika idan har Gwamnati ta saukar da Kwamishinoni za ta bayar da sanarwar haka ta hannun Sakataren watsa labari na gidan Gwamnati watau CPS, ko ta ofishin Sakataren Gwamnatin jiha, ko ta hanyar kiran taron manema labarai.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi

Top Post Ad

Below Post Ad

Shiga group dinmu na WhatsApp domin samun labaran mu kai tsaye LATSA NAN
Domin zama Wakilin mu a garin ku LATSA NAN
Domin aiko Sako/Labari/Korafi LATSA NAN
Domin samun labaran mu a Facebook LATSA NAN
Domin samun labaranmu a Twitter LATSA NAN