Saboda rashin takardun sakandire: Kotu ta yi watsi da takarar Adeleke a PDP


Legit Hausa

Kotu ta yi watsi da zaben Sanata Ademola Adeleke a matsayin dan takarar jam'iyyar PDP, a zaben gwamnan jihar Osun da aka gudanar a Satumbar 2018

Kotun ta ce Adeleke ya karya dokar sashe na 177 da ke a kundin dokar kasar da ya ce wajibi ne dan takarar gwamna ya mallaki matakin karatu har zuwa sakandire

Sai dai lauyan Adeleke ya kalubalanci wannan hukunci da mai shari'a Musa ya yanke, yana mai cewa zai daukaka kara Mai shari'a Oathman Musa a wata babbar kotu da ke da zama a karamar hukumar Bwari a Abuja a ranar Talata ta yi watsi da zaben Sanata Ademola Adeleke a matsayin dan takarar jam'iyyar PDP, a zaben gwamnan jihar Osun da aka gudanar a watan Satumba 2018.

Adeleke, wanda ke wakiltar mazabar Osun ta Yamma a majalisar dattijai, shi ne ya lashe tikitin tsayawa takarar gwamnan jihar karkashin jam'iyyar PDP a zaben gwamnan jihar Osun da aka gudanar a watan Satumba.

Wasu kusoshin jam'iyyar APC guda biyu, Wahab Raheem da Adam Habeeb, a shekarar 2018, kwanaki kadan da zaben gwamnan jihar Osun, sun maka Adeleke gaban kotu, inda suka zarge shi da gaza mallakar sahihan takardun makarantar kammala sakandire, wanda a cewarsu bai cancanta ya tsaya takarar gwamnan jihar ba.

Da ya ke yanke hukunci a ranar Talata, mai shari'a Musa, ya soke zaben Adeleke a matsayin dan takarar PDP kasancewar ya karya dokar sashe na 177 da ke a cikin kundin dokar kasar na 1999 da aka yiwa kwaskwarima.

Sashen ya ce wajibi ne dan takarar kujerar gwamna ya mallaki matakin karatu har zuwa sakandire. A cewar mai shari'a Musa, a yayin da kotun ta tattara bayanai kan cewa Adeleke ya shiga makarantar sakandire a shekarar 1976, babu wani bayani da ya nunacewa ya kammala karatun kasancewar babu sunansa a cikin kundin daliban makarantar tun daga 1980.

Mai shari'a Musa ya kara da cewa takardar kammala makarantar da ke cikin kundinsa na CF001 wanda ya gabatarwa INEC na jabu ne, saboda an samu bayanai da suka banbanta kamar yadda shugaban makarantar Ede Muslim, Ede, jihar Osun ya gabatar.

A wani labarin makamancin wannan, lauyan Adeleke, Nathaniel Oke SAN ya kalubalanci wannan hukunci da mai shari'a Musa ya yanke, yana mai cewa mai shari'ar ya fita daga hurumi ta yadda har ya samo wasu hujjoji marasa tushe da ya yanke hukuncin da babu adalci a ciki.

Ya jaddada cewa kotun ta yi biris a lokacin da aka gabatar mata da takardun WAEC na shaidar cewa Adeleke ya yi karatu har zuwa makarantar sakandire.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN