Legit Hausa
A kalla jam'iyyun siyasa 20 ne daga
jihar Zamfara su kayi karar Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta INEC a kan rashin bawa
zababen gwamnan jihar Zamfara da 'yan majalisun dokokin jihar takardun shaidan
cin zabe.
Ebenezer Adabaki ne ya shigar da
karar a ranar Talata a babban kotu da ke zamanta a Abuja a madadin masu shigar
da karar. Wadanda suka shigar da karar sun hada da Shugaban kungiyar jam'iyyun
siyasa na Zamfara, Zayyanu Haske, Zababen gwamnan jihar, Mukhtar Idris,
mataimakinsa, da zababun 'yan majalisun dokoki 24.
Masu shigar da karar suna son kotu
ta tabbatar idan sashi na 133(1) da 155 na dokar zabe ya bawa INEC ikon hana ko
rashin bayar da kula ga batun bawa 'yan takarar da suka ci lashe takardun
shedan cin zaben.
"Shin ko matakin da INEC ta
dauka na dakatar da bayar da takardan shaidan cin zabe ga 'yan takarar da suka
lashe zaben gwamna da 'yan majalisun tarayya na jihar Zamfara bai sabawa doka
ba ko kuma sakacin aiki.
" Wadanda suka shigar da karar
sun bukaci kotu ta tursasawa INEC bawa zababen gwamnan da mataimakinsa da
sauran mambobin majalisar dokokin jihar ba tare da bata lokaci ba. Sai dai a
halin yanzu ba tsayar da ranar da za a fara sauraron shari'ar.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi