Legit Hausa
Hadaddiyar kungiyar kiristocin
Najeriya tayi kira ga ilahirin kiristocin dake karamar hukumar Kajuru dasu
daina jiran dakarun Sojin Najeriya ko kuma Yansanda da nufin su karesu, su
dauki makamai su fara kare kansu kawai.
Majiyar Legit.ng ta ruwaito shugaban
kungiyar CAN, Joseph Hayab ne ya bayyana haka yayin da yake mika kayan tallafi
da uwar kungiyar CAN ta kasa ta baiwa mutanen da rikicin kabilanci dana addini
ya shafa a yankin.
“Ina kira ga yan uwana kiristoci
damu daina jiran gwamnati ta kare yankunanmu, muma zamu iya kare kanmu, idan
har zaka iya gina gidan kanka, amma kuma kana jiran Sojoji ko Yansanda su
kareka toh kana da matsala.
“Babu wata doka a Najeriya data
hanaka kare kanka, ita kawai doka ta hanaka cutar da wani ne, don haka bamuce
ku cutar da wani ba, amma ku kare kanku, kare gidanka nada goyon baya a kundin
dokokin kasa.”
Inji shi. Sai dai a wani mataki na
mi’ara koma baya kuma, Faston yayi kira ga gwamnati data kare al’ummomin da
makiyaya suka lahantasu domin su samu damar komawa gona duba da cewa damuna na
karatowa, inda ya bada tabbacin CAN zata basu abincin ci, kuma zata basu kayan
gini don sake gidajensu.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi