Legit Hausa
Adam A. Zango, jarumi a masana'antar
shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, ya kammala shiti tsaf domin angonce wa a
karo na shida cikin shekara 13. A katin gayyatar daurin auren da majiyar mu ta
gani da idonta, Zango zai angonce da wata mai suna Safiya Umar Chalawa, wacce
aka fi kira da Suffy, a ranar juma'a mai zuwa da misalin karfe 2:30 na rana.
Za a daura auren ne a masallacin
fadar sarkin Gwandu da ke garin Gwandu, a jihar Kebbi. Majiyar mu ta sanar da
mu cewar Zango ya yi aure sau biyar a baya, ya samu 'ya'ya shida; hudu maza,
biyu mata, daga mata biyar da ya aura kafin su rabu. Amina ce matar Zango ta
farko da ya aura a shekarar 2006.
Ita ce uwar yaron sa na farko,
Haidar, wanda yanzu haka ya cika shekara 12 da haihuwa. Majiyar mu ta ce ba ta
san abinda ya raba auren Zango da Amina ba. Zango ya kara auren wata matar mai
suna A'isha, 'yar asalin Shika ta karamar hukumar Zaria a jihar Kaduna.
Ta haifa masa 'ya'ya maza uku.
Jarumin ya auri matar sa ta uku mai suna Maryam daga jihar Nasarawa. Daga
bisani ya auri wata jarumar fim mai suna Maryam AB Yola a Lugbe, Abuja a
shekarar 2013. Sun bayyana tare a cikin wani shirin fim din Hausa mai suna
'Nas' A shekarar 2015, Zango ya auri Ummul Kulsum daga Ngaoundere a jamhuriyar
Kamaru.
An yi auren a sirrance. Ummul Kulsum
ce ta fara haifa wa Zango diya mace, wacce ya sanya wa suna Murjanatu. Safiyya
ko kuma Suffy kamar yadda ake kiranta, ita ce za ta kasance matar Zango ta
shida da ya aura. Majiyar mu ta ce Zango ya saki dukkan mata biyar da ya aura a
baya, sai dai har yanzu ba ta san dalilin rabuwar sa da matan da ya ke aura ba.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi