Legit Hausa
A yau Asabar dinnan ne wasu da ake
zargin barayi ne, suka kashe limamin kauyen Kwara, dake karamar hukumar Kiyawa,
cikin jihar Jigawa, hukumar 'yan sandan jihar ta tabbatar da faruwan lamarin.
Mai magana da yawun hukumar 'yan
sandan jihar, SP Abdu Jinjiri, shine ya fadawa kamfanin dillacin labarai na
Najeriya, inda ya bayyana cewa lamarin ya faru da misalin karfe 1:30 na dare.
Jinjiri ya ce marigayin mai suna, Al-Sheikh Idris Musa, mazaunin garin Kwara,
barayin sun kai masa hari a gidansa bayan ya sayar da gonarsa akan kudi naira
dubu 400, ga wani kamfanin gine-gine da ke jihar.
Ya ce wadanda ake zargin sun yi ta
dukan marigayin da itace, wanda ya yi sanadiyar mutuwarsa. Jami'in ya kara da
cewa wadanda ake zargin sun dauki kudin da marigayin ya sayar da gonar ta sa,
naira dubu dari hudu.
A cewarsa, wadanda ake zargin bayan
kashe marigayin, sun daki matanshi da 'ya'yanshi. "Ana tsammanin cewa an
yi cinikin gonar a gaban wadanda ake zargin, sai dai har yanzu ba a san su waye
ba.
"Munn dauki iyalan marigayin da
barayin suka daka munn kai su asibiti mafi kusa domin karbar magani," in
ji Jinjiri. Ya kara da cewa sun bar gawar marigayin ga iyalanshi domin ayi masa
sallah a binne shi. Ya ce, yanzu haka 'yan sanda sun fara gabatar da bincike
akan lamarin, kuma za su yi kokari wajen ganin sun kama wadanda ake zargin.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi