Legit Hausa
Jam’iyyar Peoples Democratic Party
(PDP) ta gargadi ministan shari’a, Abubakar Malami, bisa yunkurin hargitsa
gudanarwar kiduddugan kuri’un zaben gwamna da aka gudanar a ranar 9 ga watan
Maris a jihar Rivers.
Hukumar zabe na kasa mai zaman kanta
(INEC) ta dakatar da tattara sakamakon zabe saboda rikici da ya mamaye zaben.
Hukumar ta kafa ranar 2 zuwa 5 ga watan Afrilu don cigaba da kidudduga don
bayyana wanda ya lashe zaben.
A wani jawabin da kakakin PDP Kola
Ologbondiyan ya gabatar jiya, yace dole Malami ya tsare kansa kuma kada ya
yarda ayi amfani da shi wajen gudanar da ayyukan da suka saba ma doka a harkar
da ya shafi zaben Rivers Jam’iyyan ta kara gargadin Malami bisa zargin jawabin
da ministan sufuri, Rotimi Amaeci yayi, cewa Malami na aiki don baiwa shugaban
hukumar INEC, Mahmood Yakubu umurnin, tsayar da tattara sakamakon .
A wani lamari na daban, Legit.ng ta
rahoto cewa anatan jihar Zamfara ta tsakiya, Kabiru Marafa, ya bayyana cewar
gwamna Abdulaziz Yari na jihar ta Zamfara ya saba wa Allah a kan hakikicewar da
yake yi a kan cewar jam'iyyar APC ta gudanar da zaben fidda 'yan takara a
Zamfara.
Da yake amsa tambayoyin manema
labarai a kan harkokin siyasa a jihar Zamfara, Sanata Marafa ya bayyana cewar
kamata ya yi gwamna Yari ya nemi yafiyar Allah a kan yaudarar da ya yiwa
mutanen jihar Zamafara a kan batun zaben fidda 'yan takara.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi