Legit Hausa
Yan bindigan da suka addabi jihar
Zamfara sun bayyana cewa suna samun labarin dukkan wani motsi da jami'an Sojoji
ke yi na yunkurin kawo musu hari.
Wannan ya bayyana ne a wani faifan
rediyo tsakanin daya daga cikin yan barandan da wani sarkin gargajiya a jihar
Zamfara, jaridar Punch ta samu rahoto.
Ga yadda tattaunansu ya kasance:
Dan bindiga: "Allah ya riga ya
ba ka kujeran da idan kayi magana, mutane zasu ji. Wannan rikicin ya addabi
jiharmu tsawon shekaru shida kenan." "Sun kashe mutane na; sun kashe
yan uwana; sun kashe mata na da yara na. Sun kashe dabbobi na. Sai na shiga
harkar yan bindigan tunda an kashe min kowa. Amma yanzu na dawo gida, shin za
ku karbe ni a matsayin dan gari?"
Sarki: "Haka ne"
Dan bindiga: "Ka kira dukkanin
fadawanka da mutanen gari. Ka basu shawaran duk inda suka ganmu, su hada kai da
kungiyar Miyyeti Allah. Za'a samu zaman lafiya." "Idan akayi hakan,
za'a samu zaman lafiya. Amma idan kuka ce yan sanda da Soji za'a kawo Zamfara,
hakan ba zai kawo lafiya ba. Za'a cigaba da zub da jini ne."
Sarki: "Haka ne"
Dan bindiga: "Wani zubin za ka
samu labarin cewa an kai hari inda yan bindiga suke, amma gobe sai mu sake kai
hari a kusa da wajen. Dalilin da yasa bama-baman soji ba zai yi aiki ba shine
kafin jirginsu ya iso, mun samu labari."
Sarki: "Ba mu goyon bayan
hare-haren bama-baman"
Dan bindiga: "Kafin jirginsu ya
tashi daga bariki, mun samu labari. Kuma idan suka kai harin, tsuntsaye da
dabbobi kawai suke kashewa. Idan kuma aka tura sojin kasa su kawo mana hari,
tun kan su iso zamu samu labari. Muna son ka hana yan banga fitowa ga baki
daya."
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi