Legit Hausa
Wani tsohon malamin makarantar
Isolog Group of Schools, Agbole Akute dake jihar Ogun wanda ya tsere akan
zargin da akeyi masa nayin lalata da daliban makarantar ya shiga hannun hukuma.
Wanda ake zargin mai suna, Adebayo Gbadebo, ya shiga hannun hukuma ne a daren
Litinin bayan da aka matsayawa hukumar makarantar cewa lallai sai ta nemo shi,
hakan kuwa akayi. A n sanar damu cewa wanda ake zargin ya tafi ofishin yan
sanda da lauya da tunanin cewa hakan zai bashi dammar samun beli.
Jaridar The Nation that fahimci cewa
lauyan ya bukaci a sake yin wani gwajin a asibiti akan wanda abin ya faru da
ita, wanda da farko an kai ta Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jihar Legas (wato
LASUTH) yayin da ake zargin anyi batanci da yarinyar a wannan lokacin. Da yake
tabbatar da kama wanda ake zargin mai Magana da yawun rundunar yan sandan
jihar, wato DSP Abimbola Oyeyemi ya shaidawa wakilinmu cewa Kwamishinan yan
sanda ya bayar da umurnin cewa a mika wannan badakkala zuwa ga sashen dake kula
da safarar yara da kuma kare hakkin dan adam na jihar wato (SCIID) domin
gudanar da nasu binciken.
Ya tabbatar mana cewa wanda ake
zargin da lauyansa yazo inda ya bukaci a sake gudanar da wani gwajin akan
yarinyar da abin ya faru da ita sai dai ba a karbi korafin nasa ba saboda
ofishin yan sanda ba kotu bane, haka kuma baza su bar yarinyar ta shiga wani
hali ba da ka iya bata matsala har ma ya shafi lafiyarta. Oyeyemi yace: “Eh,
tabbas mutumin yana hannu kuma Kwamishina ya bada umurnin a mika shi zuwa ga
sashen kula da yancin bil adama da kuna hana safarar kananan yara domin karin
bincike.
“Sun zo tare da lauya kuma bamu amince da wasu
daga cikin bukatunsu ba. Sun nemi sake yin gwaji ga yarinyar a wani wurin gwaji
na daban, sai muka fada masu ba a kotu muke hakan ba zai samu ba, a halin yanzu
badakkalar na karkashin kulawar sashen hana safarar kananan yara da kuma kare
hakkin bil adama ta SCIID don gudunar da kwareren bincike. “Makarantar ce ta
kawo shi bayan matsin lamba daga wurin yan sanda na cewa lallai sai sun kawo
shi. Makarantar ta rufe laifin ne lokacin da abin ya faru sai dai kawai
sallamarsa da tayi shikenan."
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi