Asiri ya tonu: Yansanda sun kama makamai a ofishin APC da PDP a jihar Kano


Legit Hausa

Hukumar 'yan sandan Najeriya reshen jihar Kano, ta samu nasarar cafke wasu muggan makamai a ofisoshin jam'iyyar APC da kuma na PDP da ke karkashin karamar hukumar Tudun Wada kamar yadda rahotanni suka ruwaito.

Majiyar jaridar Legit.ng ta ruwaito cewa, hukumar 'yan sandan ta kuma samu nasarar cafke 'yan bangar siyasa takwas masu alaka da wannan muggan makamai kamar yadda kakakin 'yan sandan jihar ya bayyana, DSP Haruna Abdullahi.

Da ya ke bayar da tabbacin sa a kan wannan lamari, DSP Abdullahi ya ce muggan makamai da suka shiga hannu sun hadar da adduna, wukake, miyagun kwayoyi da kuma sauran muggan makamai masu barazana ga lafiya.

Yayin tuntubar shugaban jam'yyar APC na jihar Kano Abdullahi Abbas, ya shaidawa manema labarai cewa ba bu dan jam'iyyar APC ko guda da ya shiga hannun jami'an tsaro a sanadiyar alakar sa da makaman da ta kai hannu gare su. Cikin zayyana nasa jawabin, sakataren jam'iyyar PDP na jihar Alhaji Shehu Wada Sagagi, ya ce hukumar 'yan sanda ta bayar da belin 'ya'yan jam'iyyar su bayan da ta gaza kama su da zargin da ta ke tuhumar su.

Kazalika kwamshinan 'yan sandan jihar CP Muhammad Wakil ya bayyana cewa, ya na nan daram kan bakin aikin sa kuma an daina jin duriyar sa a halin yanzu sakamakon shudewar kakar zabe kamar yadda ya bayyana manema labarai na BBC Hausa a makon da ya gabata.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

 Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN