Legit Hausa
Mun samu labari cewa Babban kotun
daukaka kara da ke zama a Garin Kaduna ta tabbatar da takarar Injiniya Abba
Kabiru Yusuf na jam’iyyar PDP mai adawa a jihar Kano a zaben da ya gabata na
2019.
Kotu tace babu shakka Injiniya Abba
Kabiru Yusuf shi ne tabataccen ‘dan takarar PDP a zaben gwamnan jihar Kano na
bana. Kotun ta rushe hukuncin da wani Alkalin babban kotun tarayya da ke zama a
Kano yayi kwanakin baya.
Alkali mai shari’a Tanko Hussaini na
kotun daukaka karar da ke Kaduna ya bayyana cewa tun farko kotun tarayya da ke
Kano tayi kuskure da tayi watsi da takarar Abba Yusuf bayan karar da wani
Ibrahim Little ya shigar gaban ta.
Babban Alkalin kotu yake cewa Alhaji
Ibrahim Little bai da hurumin da zai kalubalanci matakin da jam’iyyarsa ta
dauka. Haka kuma Alkalin ya bayyana cewa Alhaji Little bai cikia sharudan da su
ka dace wajen shigar da kararsa ba.
Wannan ya sa mai shari’a Tanko
Hussaini ya tabbatar da takarar Abba Yusuf a PDP yana mai raba gardamar rikicin
da wasu ‘yan jam’iyyar adawar su ke yi, inda su kace ba su yarda cewa shi ne
ainihin mai rike da tutar jam’iyya ba.
A baya wani Alkali, yace ba ayi
zaben fitar da gwani a PDP ta jihar Kano ba. Jam’iyyar ta musanya wannan inda
tace Abba Yusuf ne ya zo na 1 a zaben fitar da gwaninta, sannan Jafar Bello, Sadiq
Wali da Salihu Takai su ka biyo baya.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi