Legit Hausa
Wata kungiyar sa kai mai neman
yancin al’umma, mai suna PAIR, ta dora alhakin munanan hare-haren da ake kai wa
jihar Zamfara a kan Ministan tsaro, Mansur Dan Ali, maimakon a kan Gwamna
Abdul’aziz Yari na jihar.
Baya ga PAIR kungyoyin SGE, NEO da
TPC ma sun daura alhakin a kan ministan, kuma sun ce Dan-Ali bai yin wani
gagarimin hobbasan da za a gani har a yaba cewa da gaske ya ke yi wajen ganin
an magance fitinar.
Gamayyar Kungiyoyin sun ce Yari ya
yi iyakar bakin kokarinsa da dokar kasa ta wajabta masa, ta hanyar bayar da
taimakon kayan aiki, sadarwa da bayanai, bayar da gidaje da kuma alawus na
musamman ga ‘yan sanda da sojojin da aka tura a Zamafara, ba tare da wani samun
taimako daga Ma’aikatar Tsaro ba.
A cikin wata sanarwa da Isa Yaro ya
sa wa hannu, a madadin Gamayyar Kungiyoyin, a jiya Lahadi a Abuja, ya nuna
rashin jin dadin yadda Gwamnatin Tarayya ta kasa shawo kan wannan fitina a
Jihar Zamfara sama da shekara biyu.
Isa ya ce tun tuni ya kamata a ce
Shugaba Muhammadu Buhari ya kori Ministan Tsaro, Mansur Dan Ali. Yaro ya ce ya
kamata Shugaba Muhammadu Buhari ya yi karatun ta-natsu, ya san irin mutanen da
zai nada kan mukamai idan an shiga sabon zangon mulki na biyu a ranar 29 Ga
Mayu.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi