Legit Hausa
Kungiyar kare hakkin farar hula na
Kano wato Kano Civil Society Forum ta soki zaben rabar gardama da aka gudanar a
jihar kwana-kwanan nan inda ta ce an tafka gidadanci da abin kunya ga
demokradiyar Najeriya. A sakon da kungiyar ta fitar dauke da sa hannun shugabanta
da sakataren ta, Kwamared Ibrahim A.
Waya da Peter Hassan Tijjani, tayi
ikirarin cewa anyi rikici sosai tare da razana masu zabe da kashe-kashe. A
cewar kungiyar, "Demokradiyar Najeriya yana sauyawa zuwa siyasar zalunci
inda shugabani ke amfani da amfani da karfi da razana al'umma suka zama
hanyoyin da ake amfani da su wurin samun mulki a maimakon kuri'u.
"A matayin mu na kungiyar kare
hakkin farar hula, abinda muka lura da shi a wasu rumfunan zabe ya yi kama da
yaki ne tsakanin abokan gaba biyu ba zabe tsakanin jam'iyyun siyasa biyu da
akayi bisa dokoki ba.
Kungiyar kare hakkin farar hular ta
zargi Hukumar Zabe INEC da Rundunar 'yan sanda ta fifita bangare guda a zaben
inda ta bukaci Sufeta Janar na 'yan sanda, Mohammed Adamu ya kafa kwamitin bincike
a domin gano irin rawar da suka taka a zaben.
"Abinda muka lura da shi a
zaben cike gibi na gwamna a jihar Kano shine magudi aka tafka kuma hakan babban
abin kunya ce ga demokradiyar Najeriya baki daya.
"Mun lura cewa zaben na ciki
gibi na jihar Kano da aka gudanar a ranar 23 ga watan Maris itace zabe mafi
muni. An dauko hayar 'yan daban siyasa domin su razana masu zabe su kuma tayar
da hankulin al'ummar Kano a kusa dukkan rumfunan zabe. Bai dace mu amince da
hakan ba," inji kungiyar.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi