Kotu na gab da sakin Maryam Sanda, Lauya ya ce babu kwakwarin hujjan da aka gabatar


Legit Hausa

Maryam Sanda, matar da ake zargi da kisan maigidanta, Bilyaminu Bello, ta bayyanawa kotu cewa babu laifin da ta aikata kan tuhumar da ake mata.

An gurfanar da ita tare da dan uwanta Aliyu Sanda; mahaifiyarta, Maimuna Aliyu da mai aikinsu, Sadiya Aminu, wadanda aka yiwa zargin taimakawa wajen boye hujja ta hanyar goge jinin mamacin.

Yayinda aka koma shari'ar Maryam ranar Talata, Lauyanta Olusegun Jolaawo, ya bayyanawa kotu cewa lauyoyin gwamnati basu kawo kwararan hujjojin da zai bukaci ta kare kanta ba. Ya kara da cewa duk hujjojin da lauyoyin gwamnati suka kawo an rigaya da watsi da su lokacin da shaidu ke gabatar da shaidunsu.

Saboda haka, kotu ta wanke Maryam Sanda daga zargin kisan kai. Hakazalika, lauyan mahaifiyar Maryam da dan uwanta ya bukaci kotu ta sakesu saboda lauyoyin gwamnati basu kawo kwararan hujjojin da zai bukacesu su kare kansu ba.

Amma lauyan gwamnati, Fidelis Ogbobe, ya yi kirag kotun tayi watsu da wannan bukata da lauyan Maryam keyi. Alkalin kotu, Jastis Yusuf Halilu, ya daga zaman zuwa ranar 4 ga watan Afrilu, 2019. Idan alkalin ya amsu bukatar lauyoyin dake kare wadanda ake zargi da laifi, za'a sakesu.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN