Legit Hausa
Mai Gwamnan Jihar Bauchi, Muhammad
Abubakar ya musanya rahotannin da ke yawo na cewa ya fito ya taya ‘dan takarar
jam’iyyar PDP a zaben jihar watau Bala Mohammed murnar samun nasara. Gwamnan na
Bauchi yayi wannan jawabi ne ta bakin babban Sakataren sa na yada labarai,
Abubakar Alsadique.
Dazu aka rika jin labari na yawo
cewa Gwamna Muhammad Abubakar ya saduda ya amince da shan kayi a zaben. Gwamnan
yake cewa hankalin su ya zo kan wata jita-jita da ake yi na cewa har yayi maza
ya taya Abokin hamayyar sa murna na lashe zaben da aka yi. Babban mai magana da
yawun bakin gwamnan yace babu gaskiya a labarin.
Muhammad Abubakar ya musanya wannan
rahoto da ya bi gari inda yace labari ne kurum irin na rediyo mai jini don haka
yayi kira ga jama’a su yi watsi da wannan labari. Abubakar Alsadique yace sam
bai fitar da wannan jawabi ba.
Mai magana da yawun bakin Gwamnan
yace su na da hanyoyin ganawa da manema labarai idan har za a fitar da wani
jawabi, inda yace a wannan karo gwamna bai zanta da ‘yan jarida, har yayi jawabin
taya PDP murnar cin zabe ba.
Yanzu an koma cigaba da tattara
sakamakon zaben da aka yi a cikin karamar hukumar Tafawa-Balewa da ta rage. A
zaben cike-gibi da aka yi a Ranar Asabar, jam’iyyar PDP ce ta lallasa APC mai
mulki a jihar.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi