Legit Hausa
Dakta Abdulahi Umar Ganduje, gwamnan
jihar Kano kuma dan takarar jam'iyyar APC a zaben gwamna, ya sake lashe zabe a
karo na biyu bayan an kai ruwa rana tsakaninsa da dan takarar jam'iyyar PDP,
Abba Kabir Yusuf.
Ganduje ya lashe zaben ne da
banbancin kuri'u 9,000 bayan cike gurbin kuri'un da Abba ya dora masa a zagayen
farko na zaben da aka yi a ranar 9 ga watan Maris. Sakamakon kananan hukumomi
biyu ya kawo tsaiko wajen sanar da sakamakon zaben. Kananan hukumomin su ne;
Kibiya da Nasarawa.
A karamar hukumar Kibiya, Abba Kabir
Yusuf na jam'iyyar PD ya samu kuri'u 228, yayin da Abdullahi Umar Ganduje na
jam'iyyar APC ya samu kuri'u 371.
A karamar hukumar Nasarawa, APC ta
samu adadain kuri'u 10,536, yayin da jam'iyyar PDP ta samu adadin kuri'u 3,409.
A karshen zaben raba gardama da aka
kamma jiya, Asabar, a kananan hukumomi 28, APC ta samu jimillar kuri'u 45,876
da suka ba ta rinjaye a kan jam'iyyar PDP wacce ta samu jimillar kuri'u 10,239.
A zaben ranar Asabar, 9 ga watan
Maris, da hukumar zabe ta kasa (INEC) ta bayyana cewar bai kammalu ba,
jam'iyyar PDP ce ke kan gaba da adadin kuri'u 1,014,474, yayin da jam'iyyar APC
ke da adadin kuri'u 987,817.
Yanzu bayan an kammala tare da hada
jimillar dukkan kuri'un kowacce jam'iyya daga zabukan biyu da aka gudanar, jam'iyyar
APC na da kuri'u 1,033,695 da suka ba ta nasara a kan jam'iyyar PDP, wacce ta
samu kuri'u 1,024,713.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi