Legit Hausa
Shugaban jam'iyyar APC na kasa,
Adams Oshiomhole, ya bayyana cewar mambobin jam'iyyar sa ne kadai zasu samu
mukami a majalisar tarayya in banda kujerar shugaban marasa rinjaye.
Da yake magana yayin wata ganawa da
mambobin majalisar wakilai da aka zaba a karkashin tutar jam'iyyar APC,
Oshiomhole ya ce APC zata yi amfani da rinjayen da take da shi wajen zabar
shugabannin majalisar.
Oshiomhole ya kara da cewar mambobin
jam'iyyar APC ne zasu shugabanci kwamitocin majalisar in banda shugabancin
kwamitin asusun jama'a, wanda doka ta bayyana cewar na jam'iyyar adawa ne.
An gudanar da taron ne a cibiyar
Yar'Adua da ke Abuja, birnin tarayya. "Muna da yawan mambobin da zamu
samar da kakakin majalisa, a saboda haka shugaban majalisa dole ya kasance dan
jam'iyyar APC. "Ina son ku saka a cikin zukatan ku cewar tamkar 'yan uwan
juna mu ke, za mu hada kai kamar yadda alamar tsintsiya ta jam'iyyar mu ke
nunua wa.
"Mu na da yawan zamu karbi
shugabancin majalisa kuma zamu yi amfani da yawan mu don cimma wannan buri na
mu. "Kujerar shugabanci daya ce APC za ta bari; kujerar shugaban marasa
rinjaye. Ba zamu raba mukamin shugabancin majalisa da na kwamitoci da wata
jm'iyyar ba. Da 'yan Najeriya a son wata jam'iyya ta shugabanci majalisa da sun
zabi mambobin jam'iyyar fiye da na jam'iyyar APC," a cewar Oshiomhole.
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi