Legit Hausa
Akwai alamu da ke nuna cewa jam’iyyar APC mai mulki ta tafka magudi na Inna-naha a zaben shugaban kasa da kuma ‘yan majalisun tarayya da aka yi makonni 2 da su ka wuce a Jihar Kano da fadin Najeriya.
Mun samu wannan labari ne ta wani
faifan murya inda aka ji wani da ake tunani cewa yana cikin manyan APC a jihar
Kano yana bayyanawa wani Abokin sa yadda su ka murde zabukan da aka yi a wasu
kananan hukumomi.
A sautin wayar da aka dauka, wani
babban ‘dan APC da ake ikiarin sunan sa Honarabul Kamilu, an ji yadda APC ta
murde kuri’un yankin Doguwa, Tudun Wada, Kumbotso, Kunci, Shanono, Bagwai, da
kuma Dawakin Tofa, da sauran su.
Wannan babban ‘dan APC yake
bayyanawa wani Bawan Allah da su ke waya cewa duk aringizo su kayi domin a tika
PDP da kasa. Jam’iyyar PDP dai ta gaza kawo ko da kujera guda a zaben ‘yan
majalisa 24 da kuma Sanatocin jihar.
Da bakin sa, wannan mutumi yake cewa
sun sa an rike sakamakon zaben da aka yi a yabkin karamar Hukumar Nassarawa,
Tarauni, Dala da karamar hukumar Birnin Kano ne da nufin a ba shugaba Buhari
kuri’u kamar miliyan 2.
A karshe dai hakan bai yiwu ba, inda
shugaba Muhammadu Buhari ya tashi da kuri’u sama da miliyan 1.4. Buhari ya ba
‘dan takarar PDP, Atiku Abubakar, ratar kuri’a fiye da miliyan guda a zaben,
wanda ya sa PDP tace za ta tafi Kotu.
A karshen wayar an ji wannan mutumi
yana fadin yadda APC ta ci kujerar Sanatan Kano ta tsakiya da aringizo. An
dauko muryar Hon. Kamilu yana cewa: “Wallahi tallahi an karawa Shekarau kuri’a
200, 000”
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi