Ana zargin mutum 1 ya mutu sakamakon rikin magoya bayan APC da SDP a Kakuri

An kashe mutum daya sakamakon wani hargitsi da tashin hankali a Kakuri a karamar hukumar Kaduna ta kudu a jihar Kaduna.


Rahotanni sun ce tashin hankalin ya faru ne tsakanin magoya bayan jam'iyun APC da na SDP a lokacin yawon yakin neman zabe a Kakuri ranar  Laraba 6 ga watan Maris, 2019.

Hakazalika majiyarmu ta ce rikicin ya sa matasa sun yi amfani da mugan makamai kamar wukake kuma suka ta yi ma junansu raunuka lamari da ake zargin ya kai ga mutuwar wani matshi mai suna Daniel Adamu.

Bayanai sun ce an barnata dukiyoyin jama'a, shaguna, motoci tare da yin sace--sacen ababe da dama.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN