Kazamar siyasa: 'Yan daba dauke da muggan makamai sun kai wa kwamishin Tambuwal hari

Legit Hausa

Wasu 'yan bangar siyasa wadanda ake zargin magoya bayan jam’iyyar APC ne sun kai farmaki a gidan Babban Lauyan Gwamnati kuma Kwamishinan Shari’a na Jihar Sakkwato Barista Sulaiman Usman (SAN) a yammacin jiya tare da muzgunawa jama’a.

Da yake yi wa nanema labarai bayani a Cibiyar Lauyoyi ta Gamzaki a Arkilla, Babban Lauyan Nijeriya, Barista Sulaiman Usman ya bayyana cewar a lokacin da lamarin ya faru yana wajen yakin neman zaben PDP a Karamar hukumar Kware.

A cewar sa 'yan bangar siyasar sun yi aika-aikar ne da hadin bakin wasu jami'an 'yan sandan jihar da kuma wani dan dabar da ake cewa Bashiru Marar-Guiwa.

Kwamishinan ya bayyana cewar wannan ba shine karo na farko ba da hakan ke faruwa domin kuwa hakan ta faru a baya a shekarar 2008 a filin jirgi zai je Abuja daga Sakkwato shekaru 10 da suka gabata.

Daga karshe dai, kwamishinan yayi kira ga Kwamishinan ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro a jihar da su dauki matakin da ya kamata ta hanyar zakulo wadanda lamarin ya shafa tare da hukunta su domin ya zama darasi.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN