Legit Hausa
DAGA ISYAKU.COM
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Wasu 'yan bangar siyasa wadanda ake
zargin magoya bayan jam’iyyar APC ne sun kai farmaki a gidan Babban Lauyan
Gwamnati kuma Kwamishinan Shari’a na Jihar Sakkwato Barista Sulaiman Usman
(SAN) a yammacin jiya tare da muzgunawa jama’a.
Da yake yi wa nanema labarai bayani
a Cibiyar Lauyoyi ta Gamzaki a Arkilla, Babban Lauyan Nijeriya, Barista
Sulaiman Usman ya bayyana cewar a lokacin da lamarin ya faru yana wajen yakin
neman zaben PDP a Karamar hukumar Kware.
A cewar sa 'yan bangar siyasar sun
yi aika-aikar ne da hadin bakin wasu jami'an 'yan sandan jihar da kuma wani dan
dabar da ake cewa Bashiru Marar-Guiwa.
Kwamishinan ya bayyana cewar wannan
ba shine karo na farko ba da hakan ke faruwa domin kuwa hakan ta faru a baya a
shekarar 2008 a filin jirgi zai je Abuja daga Sakkwato shekaru 10 da suka
gabata.
Daga karshe dai, kwamishinan yayi
kira ga Kwamishinan ‘yan sanda da sauran hukumomin tsaro a jihar da su dauki
matakin da ya kamata ta hanyar zakulo wadanda lamarin ya shafa tare da hukunta
su domin ya zama darasi.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi