Da dumin sa: Hukumar INEC za ta sake zaben 'yan majalisar tarayya a jahohi 14 gobe


Legit Hausa

Hukumar zabe mai zaman kan ta ta kasa a tarayyar Najeriya watau Independent National Electoral Commission (INEC) tace yanzu ta yanke shawarar ta sake gudanar da zabukan kujerun wasu 'yan majalsun tarayya a jahohi 14 a fadin kasar.

Kamar dai yadda muka samu daga hukumar, zabukan sun shafi na kujerun majalisaun dattawa guda bakwai da kuma na 'yan majalisun wakilai 24 a jahohin 14.

Legit.ng Hausa ta samu cewa shugaban hukumar ta Independent National Electoral Commission (INEC), farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana wannan matsayar ta hukumar a garin Abuja yayin wani taron masu ruwa da tsaki kan zabukan watau Inter-Agency Consultative Committee on Elections Security (ICCES).

A cewar sa, hukumar ta dauki matakin soke zabukan wasu rumfuna ne a yankunan lokacin zabukan da suka gabata sati biyu da ya wuce sakamakon hargitsi, satar akwati da kuma wasu sauran laifuffukan da suka jibinci zaben.

A wani labarin kuma, sashin dake kula da manyan laifuka na rundunar ‘yan sandan Najeriya dake Yaba, jihar Legas ya fara gudanar da bincike bisa zargin cin hanci da ake yiwa DPO mai kula da sashin Pen Cinema mai suma Harrison Nwabuisi.

Majiyarmu ta bayyana mana cewa, DPO tare da wandasu jami’an ‘yan sanda ana zargin sune da amsar na goro daga wajen mazauna unguwar Alimi Ogunyemi dake Ijeiye.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN