Legit Hausa
Kamar yadda aka sani, a yau Asabar 9
ga watan Maris ne Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta INEC ke gudanar da zabukkan
gwamnoni da 'yan majalisun jihohi a jihohi 29 na Najeriya.
Kamar yadda aka zaba, Legit.ng za ta
kasance tare da ku domin kawo muku abubuwan da ke wakana a jihohi inda a wannan
shafin za mu rika kawo muku yadda zaben ke tafiya a jihohin Sokoto, Jigawa da
Kebbi.
Daga jihar Sokoto: Tsohon gwamna
Aliyu Wamako ya kada kuri'arsa A halin yanzu dai an fara kai kayayakin zabe
zuwa rumfunan zabe kuma al'umma sun fito domin kada kuri'arsu. Manyan 'yan
takarar gwamna a jihohin sune:
Jihar Sokoto
1. Ahmad Aliyu - Jam'iyyar APC
2. Aminu Tambuwal - Jam'iyyar PDP
Rahotannin da muka samu daga jihar Sokoto ya nuna cewa wasu 'yan daba sun hana
al'umma kada kuri'a a Magajin Gari da ke karamar hukumar Sokoto ta Arewa.
Jihar Jigawa
1. Muhammadu Badaru - Jam'iyyar APC
2. Aminu Ibrahim - Jam'iyyar PDP
3. Bashir Adamu - Jam'iyyar SDP
Rahotannin da muke samu a jihar Jigawa na nuna cewa an fara gudanar da zabe a
mafi yawancin rumfunan zabe da ke jihar kuma na'urorin tantance kadin zabe wato
Card reader suna aiki yadda ya kamata.
An kuma ruwaito cewa mai martaba
Sarkin Ringim, Dr Sayyadi Mahmoud Usman (CON) ya kada kuri'arsa a garin na
Ringim. A halin yanzu mun samu rahoton cewa gwamnan jihar Jigawa mai ci,
Muhammadu Badaru ya kada kuri'arsa, ya kuma yi kira ga al'umma su gudanar da
zaben cikin zaman lafiya domin samun cigaban jihar.
JIhar Kebbi
1. Abubakar Bagudu - Jam'iyyar APC
2. Isa Galaudu - Jam'iyyar PDP
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi