Kai-tsaye: Yadda zaben gwamnoni da 'yan majalisun jiha ke gudana a Sokoto, JIgawa da Kebbi


Legit Hausa

Rahoton da Legit.ng Hausa ta samu daga jihar Jigawa sun nuna cewar an saki sakamakon karamar Babura, mahaifar gwamnan jihar, Mohammed Abubakar Badaru.

Ga sakamakon kamar haka: Karamar hukumar Babura Kujerar gwamna APC 43,601 PDP. 9,113 SDP. 1,184 Majalisar dokoki APC 26,043 PDP 4,610 Karamar hukumar Kafin Hausa Gwamna APC: 38,989 PDP: 10,133 SDP: 7,725 Rahotanni daga jihar Sokoto sun nuna cewar an saki sakamakon karamar Tambuwal, mahaifar gwamnan jihar, Aminu Waziri Tambuwal.

Ga sakamakon kamar haka: Aadadin ma su kada kuri’a:123,749 Aadadin ma su kada kuri’a da aka tantance: 75,941 Kujerar gwamna APC: 29,081 PDP: 42,830 Majalisar dokoki APC: 15,328 PDP: 24,547 Zan rugumi kaddara idan na fadi zabe - Tambuwal Gwamna Aminu Waziri Tambuwal ya ce zai rungumi kaddara ya amince da sakamakon zabe idan ya sha kaye.

A yayin da ya ke jawabi bayan kada kuri'arsa, Tambuwal ya ce Allah ne ke bayar da shugbanci su kuma al'umma kawai nasu fada ne. Kamar yadda aka sani, a yau Asabar 9 ga watan Maris ne Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta INEC ke gudanar da zabukkan gwamnoni da 'yan majalisun jihohi a jihohi 29 na Najeriya.

Kamar yadda aka zaba, Legit.ng za ta kasance tare da ku domin kawo muku abubuwan da ke wakana a jihohi inda a wannan shafin za mu rika kawo muku yadda zaben ke tafiya a jihohin Sokoto, Jigawa da Kebbi. Daga jihar Sokoto: Tsohon gwamna Aliyu Wamako ya kada kuri'arsa A halin yanzu dai an fara kai kayayakin zabe zuwa rumfunan zabe kuma al'umma sun fito domin kada kuri'arsu.

Manyan 'yan takarar gwamna a jihohin sune: Jihar Sokoto 1. Ahmad Aliyu - Jam'iyyar APC 2. Aminu Tambuwal - Jam'iyyar PDP Rahotannin da muka samu daga jihar Sokoto ya nuna cewa wasu 'yan daba sun hana al'umma kada kuri'a a Magajin Gari da ke karamar hukumar Sokoto ta Arewa. Jihar Jigawa 1. Muhammadu Badaru - Jam'iyyar APC 2. Aminu Ibrahim - Jam'iyyar PDP 3. Bashir Adamu - Jam'iyyar SDP Rahotannin da muke samu a jihar Jigawa na nuna cewa an fara gudanar da zabe a mafi yawancin rumfunan zabe da ke jihar kuma na'urorin tantance kadin zabe wato Card reader suna aiki yadda ya kamata.

An kuma ruwaito cewa mai martaba Sarkin Ringim, Dr Sayyadi Mahmoud Usman (CON) ya kada kuri'arsa a garin na Ringim.

A halin yanzu mun samu rahoton cewa gwamnan jihar Jigawa mai ci, Muhammadu Badaru ya kada kuri'arsa, ya kuma yi kira ga al'umma su gudanar da zaben cikin zaman lafiya domin samun cigaban jihar.

JIhar Kebbi 1. Abubakar Bagudu - Jam'iyyar APC 2. Isa Galaudu - Jam'iyyar PDP A halin yanzu dai an kammala zabe a mafi yawancin rufunnan zabe na jihohin Najeriya har ma an fara kirga kuri'un.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN