Legit Hausa
An fara kada kuri'a a rumfar zabe
mai lamba 003 a mazabar Rafi B a karamar hukumar Sokoto misalin karfe 8.27 Zabe
yana tafiya yadda ya kamata a karamar hukumar Sokoto ta Arewa Zabe yana tafiya
lafiya kalau a Hubare 004 (PU), a karamar hukumar Sokoto ta Arewa inda aka fara
jefa kuri'a misalin karfe 8 da rabi na safe.
An fara samun rashin jituwa a rumfar
zabe Duk da cewa ba a fara kada kuri'a ba, an fara samun rashin jituwa tsakanin
wakilan jam'iyyu a rumfar zabe mai lamba 12 (Sarkin, Adar, Atiku) inda jami'in
zaben ya ce na'urar card reader da aka bashi bata aiki yadda ya kamata.
Bayan zaben gwamnoni da aka gudanar
a ranar 9 ga watan Maris a jihohin Najeriya, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta, INEC
ta bayyana cewa zabe bai kammalu a wasu jihohi shida ba, jihohin sun hada da
Adamawa, Bauchi, Benue, Kano, Plateau and Sokoto. Hukumar ta dauki matakin ne
saboda sashi na 34 (e) na dokokin zabe da ya ce zabe ba zai kammala ba idan
tazarar kuri'un da ke tsakanin dan takarar da ya lashe zabe da mai biye masa ba
su dara adadin kuri'un da aka soke ba.
Wannan dalilin ne yasa INEC ta zabi
ranar 23 Maris domin gudanar da zaben raba gardama. A jihar Sokoto dai
jam'iyyar PDP ce ke kan gaba da kuri'u 3,412 a zaben ranar 9 ga watan Maris. A
yau kuma za a gudanar da zabe a mazabu 135 a kananan hukumomi 22 na jihar inda
ake sa ran mutane 75,403 za su kada kuri'a.
A wannan shafin zamu rika kawo muku
yadda zaben raba gardamar ke kasancewa a jihar Sokoto. A halin yanzu rahoton da
muka samu daga Punch na nuna cewa an fara kada kuri'u a rumfar zabe mai lamba
004 da ke Rijia a jihar Sokoto.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi