Legit Hausa
Kotun da ke sauraron korafe korafen
zaben gwamnan jihar Osun da ke da zama a babban birnnin tarayya Abuja ta
bayyana jam'iyyar PDP da dan takararta a zaben gwamnan jihar da aka gudanar a
shekarar 2018, Sanata Ademola Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan
jihar.
Kotun ta kuma yanke hukuncin cewa ba
jam'iyyar APC da dan takararta, Gboyega Oyetola ba ne suka lashe zaben, don
haka ta kwace nasarar da aka baiwa jam'iyyar bayan zaben jihar zagaye na biyu.
Dan takarar jamiyar APC, Gboyega Oyetola ya doke abokin takarar sa na jamiyar
adawa ta PDP, Ademola Adeleke, a zaben gwamnan jihar Osun da aka sake gudanarwa
zagaye na biyu da tazarar kuri'u 483.
Hukumar zabe mai zaman kanta INEC ta
sanar da sakamakon zaben bayan karashen zaben da aka gudanar a wasu mazabu da
aka dakatar da zaben su. Sai dai bayan sanar da sakamakon zaben, Sanata Adeleke
da jam'iyyarsa ta PDP sun garzaya kotun sauraron korafe korafen zaben gwamnan,
inda suka bayyana cewa ba su amince da sakamakon zaben ba.
Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews
Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM
Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi