Jam’iyyar APC na shirin fara zawarcin yan PDP


Legit Hausa

Wani babban jigon jam'iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki, Farouk Adamu Aliyu ya bayyana cewa jam'iyyarsu ta koyi darasi akan yadda aka gudanar da zabubbukan kasar na wannan shekarar.

A wata hira da ya yi da shafin BBC ya bayyana cewa rabuwar kan 'yan takara na daya daga cikin abubuwan da suka kawo ma jam'iyyar cikas, har zama ta fuskanci kalubale a wasu jihohi wanda hakan ya yi tasiri wajen rasa wasu kujerun gwamnoni da ma na 'yan majalisa.

Ya yi misali da jihar Ogun inda ya bayyana cewa gwamnan ya yi ungulu da kan zabo inda gwamnan jihar dan APC ne amma ya jagoranci wata jam'iyya domin ganin cewa an kada jam'iyyar APC a zaben gwamna.

Ya yi kira ga jam'iyyar APC mai mulki a kasar kan cewa a shekarar 2023 ta tabbatar an yi zaben fitar da gwani na jam'iyyar sahihi kuma ingantacce a duk fadin kasar.

Farouk wanda ya kasance tsohon shugaban marasa rinjaye a majalisar wakilai, ya ja hankalin Shugaban kasa Muhammadu Buhari akan cewa alúmman kasar sun nuna masa soyayya a duk jam'iyyar da ya shiga, saboda haka ya zama wajibi ya tabbatar da cewa APC ta dore.

Daga karshe Farouk ya kara bayyana cewa za su ci gaba da zawarcin wadanda suka sauya sheka daga jam'iyyar APC don ganin cewa an dawo da su saboda tafiya tare.

A wani lamari na daban, Legit.ng ta rahoto cewa Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce zai zabi mukarraban gwamnatinsa a wannan karon bisa la'akari da cancanta da kuma dai-daito.

DAGA ISYAKU.COM

Ku biyo mu a Facebook facebook.com/isyakunews

Latsa nan ka shiga group din mu domin samun Labaran mu ta Whatsapp >>> https://chat.whatsapp.com/CM9VNSwQfZnIDKvffzvbiM

Domin GYARA wayarka ko FLASHING ka zo SENIORA TECH shago mai lamba 50 hawa na sama, TAUSHI PLAZA, Ahmadu Bello Way Birnin kebbi
Previous Post Next Post

Celebrity Gifts

Facebook

Latsa nan ka shiga group namu na WhatsApp domin samun labarai kai tsaye https://chat.whatsapp.com/EcJXY08Ikrx63mQ7F6TJfL

Domin zama wakilinmu garinku LATSA NAN

Korafi/ Shawara/ Tuntube mu LATSA NAN